IQNA

Kungiyoyin Gwagwarmayar Falastinawa Sun gargadi Isra'ila Kan Keta Alfarmar Masallacin Quds

21:44 - April 13, 2022
Lambar Labari: 3487165
Tehran (IQNA) Kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem ya fada a jiya Talata cewa ‘yan gwagwarmaya a Gaza za su dauki matsayi idan Isra’ila ta wuce jan layi a masallacin Al-Aqsa.

Ya kara da cewa: Gaza wani bangare ne na kasar Falasdinu kuma tana bin dukkan abubuwan da ke faruwa a birnin Kudus da gabar yammacin kogin Jordan.

“Ba za mu iya ware Gaza daga sauran Falasdinu ba. , siyasa, yada labarai, diflomasiyya da sauran nau'o'in goyon bayan jama'a."

Ya ci gaba da cewa, idan ‘yan mamaya suka ketare jajayen layuka wajen ci gaba da kai hari a kan al'ummar yammacin kogin Jordan, musamman ma a garin Jenin, idan har aka ci gaba da kai hare-hare a masallacin Al-Aqsa, babu shakka aka tsallake jajayen layukan, to kuwa ‘yan gwagwarmaya a Gaza za su dauki mataki.

Ya bayyana cewa kisa da aka yi a shingayen binciken, wanda ya shafi ‘yan mata da mata, ya nuna irin laifin da Isra’ila ta aikata a cikin hotuna a fili.

Kutsa kai cikin Jenin da sauran garuruwan Yammacin Gabar Kogin Jordan wani yunkuri ne na sojojin mamaya na neman dawo da martabar jami'an tsaron Isra'ila, bayan da suka girgiza matuka sakamakon nasarar da aka samu na hare-haren daukar fansa ta hanyar sadaukarwa da wasu Falastinawa suka yi.

Ya kara da cewa, kalaman ministan tsaron Isra'ila Benny Gantz game da shirye-shiryensa na kara rura wutar rikici, wani yunkuri ne na tsoratar da gwagwarmayar Palasdinawa a Gaza da kuma hana ta goyon bayan al'ummar Yammacin Gabar Kogin Jordan da Kudus, wanda hakan ba zai yi tasiri a kan ‘yan gwagwarmaya ba.

 

https://iqna.ir/fa/news/4049037

captcha