Bayanin ya ce tuni aka sanar da iyalan wadanda suka rasu, kuma bayan kamala aikin hajji za a gudanar da jazanarsu tare da sauran alhazan da suka rasu a lokacin aikin hajjin bana a kasar saudiyya.
Ahmad Ansari shi ne shugaban bangaren kiwon lafiya na hukumar alhazan kasar Masar, ya bayyana cewa, da dama daga cikin wadanda suka rasu sakamako ne na gajiya a lokacin jifar shaidan da kuma wasu amtsaloli na rashin lafiya.
Ya ce yanzu haka dai suna shirin dawo da sauran mahajjata da suka kamala aikin hajjin zuwa gida, kuma a bana babu wata matsala da aka fuskanta ta turmutsitsi wanda ya jawo mutuwar mutane a shekaru biyu da suka gabata.